fidelitybank

El-Rufa’i da tawagarsa su sani cewa ni ne ɗan takarar shugaban ƙasa a SDP – Adewole

Date:

Jagoran jam’iyyar SDP na ƙasa, kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar jam’iyyar a zaɓen 2023, Adewole Adebayo ya ce duk wanda ya shiga jam’iyyar tasu, yana sane da aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar, kamar yadda ƴan jam’iyyar suka riga suka sani.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Arise TV, Mista Adebayo yana da ƙwarin gwiwar sake yi wa jam’iyyarsa takara a zaɓen 2027, duk kuwa da irin manyan ƴan siyasar da ake sa ran za su koma jam’iyyar.

Ɗan siyasar ya ce ba ya fargabar rasa takara, duk kuwa da samun sabbin ƴan siyasar da ke shiga jam’iyyar daga wasu jam’iyyun.

“Ai duk mutumin da yake ganin shigowar wasu jam’iyyarsa zai zame masa barazana, ba zai iya zama shugaban Najeriya ba.”

“Ku fahimci wani abu, ba na damuwa da waɗanda ke shigowa jam’iyyarmu, duk wanda ya shigo yana sane cewa ni ne zan yi wa jam’iyyar takara a 2027”, kamar yadda ya bayyana a hirar.

Kalaman na Mista Adewole na zuwa ne kwanaki bayan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai ya koma jam’iyyar ta SDP bayan ficewa daga APC.

Jagoran SDPn ya kuma yaba wa El-Rufai bisa kasancewarsa jigo a siyasar Najeriya.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp