Jagoran jam’iyyar SDP na ƙasa, kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar jam’iyyar a zaɓen 2023, Adewole Adebayo ya ce duk wanda ya shiga jam’iyyar tasu, yana sane da aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar, kamar yadda ƴan jam’iyyar suka riga suka sani.
Cikin wata hira da gidan talbijin na Arise TV, Mista Adebayo yana da ƙwarin gwiwar sake yi wa jam’iyyarsa takara a zaɓen 2027, duk kuwa da irin manyan ƴan siyasar da ake sa ran za su koma jam’iyyar.
Ɗan siyasar ya ce ba ya fargabar rasa takara, duk kuwa da samun sabbin ƴan siyasar da ke shiga jam’iyyar daga wasu jam’iyyun.
“Ai duk mutumin da yake ganin shigowar wasu jam’iyyarsa zai zame masa barazana, ba zai iya zama shugaban Najeriya ba.”
“Ku fahimci wani abu, ba na damuwa da waɗanda ke shigowa jam’iyyarmu, duk wanda ya shigo yana sane cewa ni ne zan yi wa jam’iyyar takara a 2027”, kamar yadda ya bayyana a hirar.
Kalaman na Mista Adewole na zuwa ne kwanaki bayan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai ya koma jam’iyyar ta SDP bayan ficewa daga APC.
Jagoran SDPn ya kuma yaba wa El-Rufai bisa kasancewarsa jigo a siyasar Najeriya.