fidelitybank

El-Rufa’i da tawagarsa su sani cewa ni ne ɗan takarar shugaban ƙasa a SDP – Adewole

Date:

Jagoran jam’iyyar SDP na ƙasa, kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar jam’iyyar a zaɓen 2023, Adewole Adebayo ya ce duk wanda ya shiga jam’iyyar tasu, yana sane da aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar, kamar yadda ƴan jam’iyyar suka riga suka sani.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Arise TV, Mista Adebayo yana da ƙwarin gwiwar sake yi wa jam’iyyarsa takara a zaɓen 2027, duk kuwa da irin manyan ƴan siyasar da ake sa ran za su koma jam’iyyar.

Ɗan siyasar ya ce ba ya fargabar rasa takara, duk kuwa da samun sabbin ƴan siyasar da ke shiga jam’iyyar daga wasu jam’iyyun.

“Ai duk mutumin da yake ganin shigowar wasu jam’iyyarsa zai zame masa barazana, ba zai iya zama shugaban Najeriya ba.”

“Ku fahimci wani abu, ba na damuwa da waɗanda ke shigowa jam’iyyarmu, duk wanda ya shigo yana sane cewa ni ne zan yi wa jam’iyyar takara a 2027”, kamar yadda ya bayyana a hirar.

Kalaman na Mista Adewole na zuwa ne kwanaki bayan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai ya koma jam’iyyar ta SDP bayan ficewa daga APC.

Jagoran SDPn ya kuma yaba wa El-Rufai bisa kasancewarsa jigo a siyasar Najeriya.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp