fidelitybank

El-Rufa’i da abokan hamayya sun buƙaci Majalisa ta yi watsi da dokar ta ɓaci a jihar Rivers

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El Rufai da ɗantakarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam’iyyar Labour, Peter Obi sun yi fatali da matakin Shugaban ƙasa na ƙaƙaba dokar ta-ɓaci a jihar Rivers.

El Rufai da sauran jagororin jam’iyyun hamayya sun buƙaci Majalisar dokokin Najeriya ta yi watsi da ƙudirin.

A ranar Talata ne Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers inda ya dakatar da Gwamna Siiminalayi Fubara da mataimakiyarsa da mambobin majalisar dokokin jihar.

Shi ma ɗantakarar shugaban ƙasa a 2023 ƙarkashin inuwar PDP, Atiku Abubakar, a jawabin a ya yi ranar Alhamis, ya zargi Tinubu da nuna ɓangaranci.

Atiku Abubakar ya kuma nemi Shugaba Tinubu da ya janye matakin wanda ba ya bisa kundin tsarin mulkin ƙasa sannan ya maido da zaɓaɓɓn gwamna da mataimakiyarsa da sauran mutanen da aka dakatar kan kujerarsu.

A cewarsa sun yi tur da matakin sannan sun yi kira ga ƴan Najeriya da su soki ƙudirin wanda ya saɓawa kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma dimokraɗiyya.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp