fidelitybank

El-Rufa’i bai isa ya dawo da ni SDP ba – Sule Lamido

Date:

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya yi watsi da gayyatar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi masa na komawa jam’iyyar Social Democratic Party, SDP.

Lamido ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a wata hira da BBC Hausa, inda ya bayyana gayyatar a matsayin cin fuska.

Tsohon gwamnan jihar Jigawa ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP ta kafa harsashin siyasar El-Rufai.

“Jam’iyyar da muka kafa PDP ita ce ta haifi El-Rufai. Ba ka isa ka sa mu bar PDP ba.

“Ya taba cewa babu manya a Najeriya a siyasa, amma yanzu yana kira gare mu da mu shiga shi a jam’iyyar SDP,” inji shi.

Lamido ya kuma tambayi dalilin El-Rufai na ficewa daga APC zuwa SDP da salon shugabancin sa.

Lamido, yayin da yake jaddada goyon bayansa ga jam’iyyar PDP, ya ce jam’iyyar adawa ba ta yi wani abin da zai sa ya sauya sheka ba.

El-Rufai wanda a kwanakin baya ya fice daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki zuwa SDP, ya roki shugabannin ‘yan adawa a wata hira da BBC Hausa da su koma SDP.

Ko da yake El-Rufai bai ambaci sunan Lamido ba, amma ya gayyaci manyan ‘yan adawa, da suka hada da Atiku Abubakar, da Peter Obi, da Rotimi Amaechi, da Rauf Aregbesola, da su shiga jam’iyyar SDP.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp