Jam’iyyar APGA za ta gudanar da zabukan fitar da gwani na gwamna a jihohin Ekiti da Osun a ranakun 27 ga watan Janairu da 10 ga watan Maris.
A cikin wani jadawalin ayyuka na wucin gadi wanda Sakataren kungiyar, APGA na kasa, Mista Ifeanyi Mbaeri, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce za a samu fom din nuna sha’awa a kan kudi Naira miliyan 2, yayin da za a sayar da fom din tsayawa takara a kan Naira miliyan 10.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Bisa ikonta a karkashin sashi na 12 (3) da na 24 na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APGA na 2019, da kuma bin jadawalin INEC da jadawalin ayyukan zaben gwamnonin jihohin Ekiti da Osun na 2022, kwamitin ayyuka na kasa (NWC) na Jam’iyyar (APGA) ta amince da jadawalin gudanar da zaben fidda gwani na gwamnonin jihohin Ekiti da Osun a 2022.
“Za a gudanar da zaben fidda gwani na jihar Ekiti a ranar 27 ga Janairu, 2022, yayin da zaben firamare na jihar na musamman zai gudana a Osogbo, jihar Osun a ranar 10 ga Maris, 2022.”
APGA ta ce masu neman takarar bangaren mata da masu fama da nakasa su biya kashi 50 cikin 100 kawai na kudaden da aka tanada na duka fom na nuna sha’awa da na takara.
Karkashin jadawalin da a ka amince da zaben fidda gwani na Ekiti, za a gudanar da siyar da fom na nuna sha’awa da na takara a sakatariyar jam’iyyar APGA ta kasa da ke Abuja tsakanin 20 ga Disamba zuwa 10 ga watan Janairu, 2022.
A ranar 28 ga watan Junairu ne za a yi shawarwarin daukaka kara/hukumomin da suka taso daga zaben fidda gwani na Ekiti.