fidelitybank

Ekiti da Osun: APGA ta fara sayar da fom din takarar Gwamna

Date:

Jam’iyyar APGA za ta gudanar da zabukan fitar da gwani na gwamna a jihohin Ekiti da Osun a ranakun 27 ga watan Janairu da 10 ga watan Maris.

A cikin wani jadawalin ayyuka na wucin gadi wanda Sakataren kungiyar, APGA na kasa, Mista Ifeanyi Mbaeri, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce za a samu fom din  nuna sha’awa a kan kudi Naira miliyan 2, yayin da za a sayar da fom din tsayawa takara a kan Naira miliyan 10.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Bisa ikonta a karkashin sashi na 12 (3) da na 24 na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APGA na 2019, da kuma bin jadawalin INEC da jadawalin ayyukan zaben gwamnonin jihohin Ekiti da Osun na 2022, kwamitin ayyuka na kasa (NWC) na Jam’iyyar (APGA) ta amince da jadawalin gudanar da zaben fidda gwani na gwamnonin jihohin Ekiti da Osun a 2022.

“Za a gudanar da zaben fidda gwani na jihar Ekiti a ranar 27 ga Janairu, 2022, yayin da zaben firamare na jihar na musamman zai gudana a Osogbo, jihar Osun a ranar 10 ga Maris, 2022.”

APGA ta ce masu neman takarar bangaren mata da masu fama da nakasa su biya kashi 50 cikin 100 kawai na kudaden da aka tanada na duka fom na nuna sha’awa da na takara.

Karkashin jadawalin da a ka amince da zaben fidda gwani na Ekiti, za a gudanar da siyar da fom na nuna sha’awa da na takara a sakatariyar jam’iyyar APGA ta kasa da ke Abuja tsakanin 20 ga Disamba zuwa 10 ga watan Janairu, 2022.

A ranar 28 ga watan Junairu ne za a yi shawarwarin daukaka kara/hukumomin da suka taso daga zaben fidda gwani na Ekiti.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp