Shugaban hukumar yaki da yi wa tattalin arziki zagon kasa a Najeriya EFCC, Ola Olukoyede ya bayar da umarnin a gaggauta bincike kan zargin cin hanci da rashawa da Idris Okuneye wanda aka fi sani da Bobrisky ya yi a kan wasu jami’an hukumar.
Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa Bobrisky ya bayyana a wani faifan bidiyo inda ya zargi wasu jami’an hukumar waɗanda bai bayyana sunansu ba sun nemi Naira miliyan 15 daga wajensa domin dakatar da binciken da ake yi a kan sa kafin a tura shi gidan yari.
Wannan ya sa shugaban hukumar ya kafa kwamitin bincike domin tabbatar da gaskiya ko akasin zargin.
EFCC ta koma gayyaci Okuneye zuwa ofishinta na Legas domin taimakawa wajen gudanar da binciken.
A wata sanarwa da kakakin hukumar, Dele Oyewale ya fitar, ya tabbatar da cewa za a bincika zargin, sannan za a fitar da sakamako idan an kammala binciken.