fidelitybank

EFCC ta yi harbe-harbe a iska don kama Yahaya Bello

Date:

Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun killace gidan gwamnatin Kogi da ke Asokoro a daren Laraba a wani yunkurin kama tsohon Gwamna Yahaya Bello da karfin tsiya.

Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na Bello, Ohiare Michael ya fitar, ta ce jami’an EFCC na harbe-harbe kai-tsaye.

Michael, yayin da yake yin Allah wadai da harin, ya bukaci ‘yan Najeriya da su dorawa EFCC alhakin idan wani abu ya faru da Bello.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun zo mana cewa a halin yanzu mutanen da ake zargin jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ne ke kewaye da Gidan Gwamnatin Jihar Kogi, Asokoro, a kokarin da suke na kama tsohon Gwamna Yahaya Bello da karfin tsiya. Suna harbe-harbe kai tsaye.

“Muna so mu sanya shi a rubuce cewa ya kamata a tuhumi EFCC idan wani abu ya same shi.

“Harin na daren yau bai kamata ba, domin tsohon gwamnan ya mika kansa ga hukumar EFCC a ofishinsu domin yi masa tambayoyi. EFCC ba ta da tambayoyi da za ta yi wa Alh. Yahaya Bello da safe, amma kwatsam, sun fito su kama shi.

“Wannan matakin abin la’akari ne. Sun bayyana dalilin da ya sa da yawa ‘yan Najeriya ke ganin suna fada da fadace-fadacen siyasa a maimakon wa’adin yaki da cin hanci da rashawa. Wannan mataki ya nuna fiye da yaki da cin hanci da rashawa. Za mu ci gaba da sanyawa ‘yan Najeriya bayanan.”

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp