Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun killace gidan gwamnatin Kogi da ke Asokoro a daren Laraba a wani yunkurin kama tsohon Gwamna Yahaya Bello da karfin tsiya.
Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na Bello, Ohiare Michael ya fitar, ta ce jami’an EFCC na harbe-harbe kai-tsaye.
Michael, yayin da yake yin Allah wadai da harin, ya bukaci ‘yan Najeriya da su dorawa EFCC alhakin idan wani abu ya faru da Bello.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun zo mana cewa a halin yanzu mutanen da ake zargin jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ne ke kewaye da Gidan Gwamnatin Jihar Kogi, Asokoro, a kokarin da suke na kama tsohon Gwamna Yahaya Bello da karfin tsiya. Suna harbe-harbe kai tsaye.
“Muna so mu sanya shi a rubuce cewa ya kamata a tuhumi EFCC idan wani abu ya same shi.
“Harin na daren yau bai kamata ba, domin tsohon gwamnan ya mika kansa ga hukumar EFCC a ofishinsu domin yi masa tambayoyi. EFCC ba ta da tambayoyi da za ta yi wa Alh. Yahaya Bello da safe, amma kwatsam, sun fito su kama shi.
“Wannan matakin abin la’akari ne. Sun bayyana dalilin da ya sa da yawa ‘yan Najeriya ke ganin suna fada da fadace-fadacen siyasa a maimakon wa’adin yaki da cin hanci da rashawa. Wannan mataki ya nuna fiye da yaki da cin hanci da rashawa. Za mu ci gaba da sanyawa ‘yan Najeriya bayanan.”