fidelitybank

EFCC ta yi dirar mikiya a gidan Rochas

Date:

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arziki zagon kasa a Najeriya, EFCC, ta yi dirar mikiya a gidan tsohon gwamnan jihar Imo, kuma daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar APC mai mulki Rochas Okorocha.

Jaridar Punch ta rawaito cewa jami’an EFCC sun dira gidan Mr Okorocha da ke babban birnin kasar Abuja ranar Talata, sai dai kawo yanzu babu tabbacin abin da ya kai su gidan, amma daya daga cikin tsofaffin masu bai wa Okorocha shawara ya tabbatar wa jaridar tabbas jami’an sun shiga gidan.

Shi ma gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa, jami’an EFCC sun je gidan Rochas da nufin kama shi.

A bidiyon da Channels din ta samu, ya nuna jami’an EFCC suna kai komo a farfajiyar gidan tsohon gwamnan. Sun kafe sai dan takarar shugaban kasa ya fito sun cafke shi, ko kuma ya mutunta tsohon goron gayyatar da hukumar ta aika masa, da ya ki zuwa.

Jami’an sun sanya shinge a hanyar da za ta sada mutum da gidan Okorocha, kamar yadda suka bayyana jami’an EFCC sun ce babu wanda zai fita daga gidan har sai Okorocha ya mika kan shi gare su.

Ba da jimawa ba, aka ga motocinsu na ficewa daga unguwar.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp