Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, ta ce, za ta tura jami’anta zuwa jihohi 36 na faɗin kasa don sa ido a zaɓen ƙasar da za a gudanar.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na twita, shugaban hukumar Abdulrasheed Bawa, ya hori jami’an da su sanya buƙatar ƙasa a farko da kuma nuna ƙwarewa yayin gudanar da aikinsu.
“An tura ku ne don ku je ku yi wa ƙasa aiki, a don haka, ya kamata ku kasance yanda ake bukata ta hanyar nuna ƙwarewa da kuma aiki da dokokin hukumar,” in ji Bawa.
Ya ƙara da cewa suna da alhakin tabbatar da cewa ba a yi maguɗi ba a wannan zaɓe, musamman ma bai wa masu zaɓe kuɗi.
Ya ce akwai buƙatar su yi abin da ya kamata saboda idon duniya ya koma kan Najeriya na ganin an gudanar da zaɓe cikin gaskiya da lumana.