fidelitybank

EFCC ta tuhumi tsohon gwamna da kaucewa kotu a kan zarginsa da wawushe biliyan 40

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, a ranar Alhamis a babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta zargi tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Maduabuchi Obiano da kaucewa ayyukan kotu a kan zargin zamba Naira biliyan 40 da ake zarginsa da shi.

Babban Lauyan Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, kuma Babban Lauyan Najeriya, SAN, Sylvanus Tahir ya yi wannan zargin ne a yayin da ake ci gaba da shari’ar tsohon Gwamnan kan zargin cin hanci da rashawa da ake yi masa.

Tahir ya sanar da mai shari’a Inyang Edem Ekwo cewa bisa bin umarnin da kotun ta bayar a ranar Litinin, ya shigar da kara kotu na adawa da yunkurin Obiano na kalubalantar hurumin kotun na tuhumar sa.

Sai dai babban lauyan, ya koka da yadda kokarin da aka yi na mika wa tsohon gwamnan takardar shaida ta hannun lauyansa a ranar Laraba kamar yadda kotu ta umarta ya ci tura.

Ya shaida wa Kotun cewa tawagarsa ta kasance a ranar Laraba a Chamber of Dr Onyechi Ikpeazu SAN, lauyan mai ba da shawara ga Obiano amma an kulle kofar ofishin.

Tahir ya ce shi da kan sa ya buga waya da biyu daga cikin lauyoyin da ake kara amma an shaida masa cewa suna kotun sauraron kararrakin zaben gwamna.

Lauyan ya yi ikirarin cewa saboda yanayin da ake ciki, ya samu damar ba da takardar shaida ga wanda ake kara a cikin dakin kotun ranar Alhamis.

Ya roki kotun da ta ci gaba da sauraron bukatar tsohon gwamnan na kalubalantar hurumin kotun tare da karar da aka shigar.

Sai dai Patrick Ikweto SAN wanda ya wakilci Obiano a zaman da aka yi a ranar Alhamis ya tabbatar da cewa an yi masa shari’a kuma ya roki a dage shi don ba shi damar amsa karar da EFCC ta yi masa.

Mai shari’a Ekwo ya amince da bukatar sannan ya sanya ranar 13 ga watan Maris domin sauraron karar Obiano kan yankin.

An gurfanar da tsohon gwamnan, wanda ya yi wa’adi biyu a jihar Anambra, a gaban kotu bisa zargin almubazzaranci da kudaden jihar da suka kai Naira biliyan 40.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp