fidelitybank

EFCC ta kwace fasfo din Sadiya da Edu da Halima

Date:

Hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasa ta karɓe fasfon tafiye-tafiye na ministar jin ƙai da aka dakatar, da kuma na wadda ta gabace ta, wato Sadiya Umar Farouq, waɗanda ake ci gaba da bincike a kansu kan zargin aikata ba daidai ba, da dukiyar al’umma.

Haka kuma, EFCC ta kwace fasfo ɗin Halima Shehu, shugabar hukumar ba da tallafin dogaro da kai NSIPA – wadda ita ma aka dakatar bisa zargin almubazaranci da kuɗin da suka kai naira biliyan 44 da miliyan 800 a ƙarƙashin ma’aikatar jin ƙai,.

EFCC ta ce ta kwato naira biliyan 39.8 cikin biliyan 44.8 da ake zargin Halima ta yi sama da faɗi da su.

A ranar Talata ne, hukumar ta tsare Betta Edu tare da yi mata tambayoyi tsawon kusan awa 10 a Abuja. An yi mata tambaya ne kan kuɗin da suka kai miliyan 585 na hukumar.

A yau Laraba ne ake tsammanin Sadiya da Betta da kuma Halima za su sake gurfana gaban hukumar domin ci gaba da yi musu tambayoyi.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp