Hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasa ta karɓe fasfon tafiye-tafiye na ministar jin ƙai da aka dakatar, da kuma na wadda ta gabace ta, wato Sadiya Umar Farouq, waɗanda ake ci gaba da bincike a kansu kan zargin aikata ba daidai ba, da dukiyar al’umma.
Haka kuma, EFCC ta kwace fasfo ɗin Halima Shehu, shugabar hukumar ba da tallafin dogaro da kai NSIPA – wadda ita ma aka dakatar bisa zargin almubazaranci da kuɗin da suka kai naira biliyan 44 da miliyan 800 a ƙarƙashin ma’aikatar jin ƙai,.
EFCC ta ce ta kwato naira biliyan 39.8 cikin biliyan 44.8 da ake zargin Halima ta yi sama da faɗi da su.
A ranar Talata ne, hukumar ta tsare Betta Edu tare da yi mata tambayoyi tsawon kusan awa 10 a Abuja. An yi mata tambaya ne kan kuɗin da suka kai miliyan 585 na hukumar.
A yau Laraba ne ake tsammanin Sadiya da Betta da kuma Halima za su sake gurfana gaban hukumar domin ci gaba da yi musu tambayoyi.