fidelitybank

EFCC ta kama tsohuwar kakakin majalisa da almundahanar miliyoyin Naira

Date:

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta cafke tsohuwar kakakin majalisar wakilai, Patricia Etteh.

Jaridar Guardian ta tattaro a daren jiya cewa, sashen ayyuka na musamman na EFCC na tuhumar Etteh, bisa zarginta da hannu a badakalar samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a jihar Akwa Ibom.

A cewar manyan majiyoyin EFCC, “An kama ta ne kan wata kwangilar Neja-Delta (NDDC) a shekarar 2011. kwangilar aikin samar da hasken rana ne a yankunan karkara na wasu al’ummomi a Akwa Ibom. An bayar da kwangilar ne ga wani kamfani mai suna Philjim Projects Limited

Kudaden kwangilar Naira miliyan 240 ne hukumar NDDC ta bayar a wani bangare na ayyukan ci gaban al’umma. An fara sakin Naira miliyan 34, sai kuma Naira miliyan 253, wanda ya kai Naira miliyan 287 da aka biya.

“Damuwarmu akan wannan lamari shine Etteh ba darakta ba tace kuma ‘yar kwangila ba ce, amma binciken mu ya nuna cewa, ‘yar kwangilar ta biya ta jimillar kudi naira miliyan 130.

“Lokacin da masu bincikenmu suka tunkare ta da wadannan kudade, sai ta ce bashin ne da ta baiwa dan kwangilar da ke gudanar da aikin.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaÉ“en 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...
X whatsapp