fidelitybank

EFCC ta kama Mutumin da yake watsa kudin Naira a Gombe

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, shiyar jihar Gombe, ta kama wani mutum mai suna Zakariya Muhammad, da laifin watsa takardar Naira, al’adar da ake ganin tamkar cin zarafin kudin kasar nan.

Kamen dai ya biyo bayan bayanan sirri da ke alakanta Muhammad da aikata laifin, wanda ya faru a Tunfure dake jihar Gombe.

Hukumar EFCC ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Larabar da ta gabata cewa, an gano Muhammad ne a wani faifan bidiyo inda aka gan shi yana rawa yana watsa ‘yan Naira 200.

A cewar sanarwar, Muhammed ya amince da cewa, shi ne mutumin a cikin faifan bidiyon da aka yi masa tambayoyi.

Sanarwar ta ce, za a gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike.

Dokar Babban Bankin kasa (CBN), musamman sashe na 21, ta yi haramta cin zarafin Naira.

Dokar ta tanadi hukuncin daurin akalla watanni shida a gidan ajiya da gyaran hali, ko kuma tarar da ta fara daga Naira 50,000 ga wadanda suka aikata laifin.

 

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp