fidelitybank

EFCC ta kama mutane a Kano da Abuja da Kaduna

Date:

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya (EFCC), ta kama wata mata da katunan zaɓe 18 a jihar Kaduna da kuma wasu a Kano da Abuja.

Jami’an hukumar ne suka kama matar da safiyar yau a unguwar Badarwa da ke Kaduna bayan kai wani samame.

An kuma samu wata takarda ɗauke da jerin sunayen masu zaɓe guda 17 da asusun ajiyarsu na banki da lambobinsu na waya a matsayin waɗanda ke da damar yin zaɓe a mazaɓar Badarwa/Malali 01 da 08 da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa.

An kama ta ne lokacin da jami’an na EFCC suka bad-da-kama, inda suka nuna cewa za su sayar da katunansu na zaɓe.

A halin yanzu dai tana hannun jami’an na EFCC a shiyyar Kaduna, inda suke ƙoƙarin gano wasu mutane da ke tare da ita waɗanda ta ce su ma suna karɓar katunan zaɓen mutane da kuma ba su kuɗi ta amfani da POS da kuma tura kuɗin ta intanet.

A Kano kuma EFCC ta ce, ta kama wani mutum da take zargi da sayen kuri’u, inda suka same shi da tsabar kuɗi naira 194,000 a rumfar zaɓen Gidan Zakka da ke Goron Dutse a karamar hukumar ƙwaryar birnin Kano.

A Abuja kuma hukumar ta ce ta yi nasarar kama wakilin wata jam’iyya yana sayen kuri’u a karamar hukumar Abaji na babban birnin tarayya, ta hanyar tura musu kuɗi ta intanet.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp