fidelitybank

EFCC ta kama Mutane 792 da suke damfara ta Intanet

Date:

Shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya, EFCC,Ola Olukoyede, ya bayyana cewa hukumar ta kama mutum 792 da ake zargi da aikata laifin damfara ta Intanet da suka gada da damfara ta hanyar soyayya.

An gabatar da wadanda ake zargin ne a ranar Talata, 10 ga watan Disamba, 2024, yayin wani samame da jami’an hukumar suka kai a maɓoyar wadanda ake zargin, a cikin wani katafaren gini dake lamba bakwai, Oyin Jolayemi Street, Victoria Island, Lagos, bayan hukumar ta samu bayanan sirri.

Da yake jawabi ga manema labarai, Olukoyede, a ranar Litinin, 16 ga watan Disamba, 2024, a ofishin hukumar dake Lagos ya bayyana cewa cikin wadanda aka kama akwai yan Chana 148, da mutum 40 ƴan ƙasar Filipinos da kuma ƴan Kharzartans biyu, sai ɗan Pakistan da ɗan Indonesia.

Shugaban wanda ya samu wakilcin Diraktan hulda da jama’a na hukumar, CE Wilson Uwujaren, ƴan ƙasashen wajen na amfani da ginin a matsayin wajen da suke koyar da ƴan Najeriya yadda ake damfara ta Intanet musamman ta hanyar soyayya, “Ƙasa a cikin ginin an cika shi da manyan kamfutoci”, in ji shi.

“A hawa na biyar, masu binciken sun gano layukan waya 500 da wayoyin sadarwa da aka tana da domin gudanar da ayyukan ta’addanci, ana amfani da ƴan Najeriyar wajen yaudarar ƴan ƙasashen waje yawanci ƴan Amurka da Canada da Mexico da wasu ƙasashen Turai da dama.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp