fidelitybank

EFCC ta kama Mutane 792 da suke damfara ta Intanet

Date:

Shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya, EFCC,Ola Olukoyede, ya bayyana cewa hukumar ta kama mutum 792 da ake zargi da aikata laifin damfara ta Intanet da suka gada da damfara ta hanyar soyayya.

An gabatar da wadanda ake zargin ne a ranar Talata, 10 ga watan Disamba, 2024, yayin wani samame da jami’an hukumar suka kai a maɓoyar wadanda ake zargin, a cikin wani katafaren gini dake lamba bakwai, Oyin Jolayemi Street, Victoria Island, Lagos, bayan hukumar ta samu bayanan sirri.

Da yake jawabi ga manema labarai, Olukoyede, a ranar Litinin, 16 ga watan Disamba, 2024, a ofishin hukumar dake Lagos ya bayyana cewa cikin wadanda aka kama akwai yan Chana 148, da mutum 40 ƴan ƙasar Filipinos da kuma ƴan Kharzartans biyu, sai ɗan Pakistan da ɗan Indonesia.

Shugaban wanda ya samu wakilcin Diraktan hulda da jama’a na hukumar, CE Wilson Uwujaren, ƴan ƙasashen wajen na amfani da ginin a matsayin wajen da suke koyar da ƴan Najeriya yadda ake damfara ta Intanet musamman ta hanyar soyayya, “Ƙasa a cikin ginin an cika shi da manyan kamfutoci”, in ji shi.

“A hawa na biyar, masu binciken sun gano layukan waya 500 da wayoyin sadarwa da aka tana da domin gudanar da ayyukan ta’addanci, ana amfani da ƴan Najeriyar wajen yaudarar ƴan ƙasashen waje yawanci ƴan Amurka da Canada da Mexico da wasu ƙasashen Turai da dama.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp