fidelitybank

EFCC ta gurfanar da Stella a kan harƙallar kuɗaɗe

Date:

Hukumar Yaki da cin hanci da yi wa tattalin arziki Ta’annati EFCC, ta gurfanar da tsohuwar ministar sufurin jiragen sama ta Najeriya Stella Oduah, tare da wasu mutum takwas a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, bisa zargin almundahanar kuɗaɗe.

An gurfanar da mutanen ne kan zarge-zarge 25 da suka haɗa da halasta kuɗin haram, da haɗin baki, tare da amfani da wani asusun ajiyar banki marar suna a bankin First Bank da aka samu kimanin naira biliyan biyar a cikinsa.

Sai dai bayan karanto musu zarge-zargen Oduah tare da sauran mutanen takwas ciki har da wata tsohuwar hadimarta, sun musanta duka zarge-zargen da hukumar ke yi musu.

Alkalin kotun, Mai shari’a Inyang Ekwo ya umarci ofishin babban Atoni-Janar na ƙasa da ya karbi hurumin shigar da ƙarar daga hannun hukumar ta EFCC.

Stella Oduah ta riƙe muƙamin ministar sufurin jiragen sama a lokacin gwamnatin shugaba Goodluck Jonathan tsakanin shekarar 2011 zuwa 2014.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp