fidelitybank

EFCC ta gurfanar da Miji da Mata da suka damfara ƴan canji da sunan Matar Gwamna

Date:

Hukumar EFCC, mai yaƙi da almundahana a Najeriya ta gurfanar da wata mata da mijinta bisa zargin sojan gona da sunan mai ɗakin gwamnan jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Radda domin damfar kuɗin da suka kai naira miliyan 197,750,000.

EFCC ta gurfanar da su a gaban babbar kotun jihar Kaduna tare da wasu mutum biyu da ke taimaka musu wajen gudanar da mugunyar sana’ar.

Hukumar ta zargi mutanen huɗu da haɗin baki wajen damfarar waɗannan kuɗaɗe ta hanyar fakewa da sunan mai ɗakin gwamnan Katsina, da nufin neman canjin dala.

EFCC ta zargi matar da ayyana kanta a matsayin Fatima Dikko Radda, inda take buƙatar a yi mata canjin dala, daga wani mai sana’ar canji.

Mijin nata, ya samar mata da layukan waya da aka yi wa rajista da sunan Fatima Dikko Radda, domin ɓad-da-bami ga manhajar ‘True Caller’ da ke gano sunan mai lambar waya, a cewar EFCC.

Bayan ta buƙaci yi matan canjin dalar ne, sai suka tura wa mai canjin lambar asusun ajiyar da zai tura kuɗin kafin ta aika masa da dalar, kamar yadda hukumar ta bayyana.

EFCC ta ce da farko matar, ta karbi naira miliyan 89 daga wani mai suna Aminu Usman da nufin tura masa dala 53,300.

Daga baya kuma ta sake karɓar naira miliyan 108 da nufin canja mata dala 118 da ta ce za ta aika masa, kamar yadda EFCCn ta bayyana.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp