fidelitybank

EFCC ta gurfanar da Magatakardar kotu da karkatar da Naira miliyan 3.8 na magada

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, ta gurfanar da tsohon magatakardar Kotun Shari’ar Musulunci ta Jihar Zamfara 1, Gusau, Abubakar Garba Dandare, a gaban Mai Shari’a Bello Shinkafi na Babbar Kotun Jihar Zamfara da ke Gusau.

Hukumar ta gurfanar da Dandare ne a kan tuhume-tuhume biyu, inda ta zarge shi da karkatar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 3.8 na wani dan kasuwa marigayi Alhaji Ladan Mada da kuma jabun sa hannun makusancinsa, Aminu Mada.

A cikin karar mai lamba ZMJ/GS/13C/2024, Dandare an tuhumi shi ne da laifin karkatar da N3,837,634.46, wanda ma’aikatar kudi ta jihar Zamfara ta bashi amanar iyalan marigayi Alhaji Ladan Mada a watan Disambar 2012, lokacin yana magatakardar hukumar. Upper Sharia Court 1, Samaru Gusau, Zamfara State.

An kuma zargi Dandare da yin jabun sa hannun Aminu Mada, dan gidan marigayi Alhaji Mada, a rajistar ajiyar kudi na kotun shari’a ta 1, Samaru Gusau, jihar Zamfara, da nufin samun kudaden.

Hukumar ta EFCC ta bayyana cewa, matakin ya kunshi laifukan cin amana, kamar yadda aka bayyana a sashe na 311 da 312 na Penal Code, CAP 89 Laws of Northern Nigeria, 1963.

Mai shari’a Bello Mohammed Shinkafi ya bayar da belin wanda ake tuhuma, bisa sharadin ya bayar da wadanda za su tsaya masa guda biyu mazauna jihar, a kan kudi naira miliyan biyar.

Kuma dole ne su mika fasfo dinsu da lambobin GSM guda biyu ga magatakardar kotu

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp