fidelitybank

EFCC ta gurfanar da Kakakin majalisar jihar Ondo a kotu

Date:

Hukumar da ke Yaƙi da yi wa Tattalin Arzikin Ta’annati EFCC, ta gurfanar da kakakin majalisar jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya, Rt. Hon. Bamidele Oloyeloogun a gaban babbar kotun jiha da ke Akure.

Ana zargin ɗan majalisar tare da wasu mutum biyu da zambar ƙuɗaɗe, zargin da duka mutanen suka musanta.

Lauyan hukumar EFCC Kingsley Kudus, ya nemi kotun da ta ajiye mutanen uku a gidan gyaran hali na Akure yayin da ake ci gaba da shari’ar.

Ya ce duk da cewa mutanen sun musanta zargin da ake yi musu, har yanzu suna ƙarƙashin kulawar kotu yayin da ake ci gaba da shari’ar.

Lauyan waɗanda ake zargin Barrister Femi Emodamori ya shaida wa kotun cewa a shirye yake domin fara shari’ar gadan-gadan.

Ya kuma nemi kotun da ta yi watsi da buƙatar ajiye waɗanda yake karewar a gidan gyaran hali, kamar yadda lauyan EFCCn ya buƙata, yana mai cewa takardar nemin belin da suke cike tana kan ƙa’ida.

Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin mutanen da yake karewa na fama da rashin lafiyar da ke buƙatar kulawar gaggawa.

Daga ƙarshe dai alƙalin kotun mai shari’a Adegboyega Adebusoye ya bayar da belin mutunen tare da ɗage shari’ar zuwa ranar 18 ga watan Mayu mai zuwa.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp