fidelitybank

EFCC ta gurfanar da Emefiele a gaban kotu

Date:

A ranar Laraba ne Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, a Abuja, ta bi umurnin babbar kotun tarayya da ke birnin tarayya Abuja kan shari’ar tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele.

Emefiele wanda ya shafe sama da kwanaki 150 a hannun hukumomin tsaro na gwamnatin tarayya an gurfanar da shi a gaban kotu bisa bin umarnin mai shari’a Olukayode Adeniyi.

Tsohon Gwamnan Babban Bankin na CBN wanda ya sa rigar Babariga mai launin rawaya da hular Hausa don daidaitawa ya shiga harabar da misalin karfe 12:30 tare da wasu jami’an EFCC da ke ba da tsaro a kusa da shi.

Abokansa da ’yan uwansa sun yi wa harabar kotun kawanya suna jiran isowar alkali domin sauraren shari’ar sa na kare hakkin bil adama.

Mai shari’a Adeniyi a ranar Litinin din da ta gabata ya sake tabbatar da umarninsa na cewa a gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin na CBN a kotu a yau 8 ga watan Nuwamba domin bada belinsa.

Ya kuma umurci hukumar yaki da cin hanci da rashawa da kanta da ta bayar da belin Emefiele ko kuma ta bar kotu ta yi hakan kamar yadda doka ta tanada kan hakkin dan adam.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp