Hukumar Yaki da masu yi wa Tattalin Arzikin kasa ta’annati EFCC ta gano ƙarin naira miliyan 900 na hukumar Inshorar Lafiya ta NHIS.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN ya ambato mai magana da yawon hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren na bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.
Mista Uwujaren, ya yi zargin cewa kuɗin wani ɓangare ne da wasu bankunan ƙasar suka riƙe tun 2015 suka ƙi sanya wa a asusun hukumar Inshorar Lafiyar ƙasar wato NHIS.
Ya ƙara da cewa a yanzu an tura kuɗin zuwa asusun na NHIS.
Ya ci gaba da cewa a ranar 10 ga watan Fabrairun 2022, hukumarsu ta EFCC ta sakar wa NHIS ɗin naira biliyan 1.5 da ta kwato daga bankunan.
Haka kuma a ranar 5 ga watan Agustan 2022, EFCC ta ƙara sakar wa NHIS naira biliyan 1.4
A baya dai babban sakataren hukumar NHIS Farfesa Muhammad Nasir Sambo, ya sha yabawa da ƙwazon hukumar ta EFCC wajen taimaka wa NHIS ƙwato kuɗadenta da suka maƙale a wasu bankunan kasuwancin ƙasar.