fidelitybank

EFCC ta gano Naira miliyan 900 a hukumar NHIS

Date:

Hukumar Yaki da masu yi wa Tattalin Arzikin kasa ta’annati EFCC ta gano ƙarin naira miliyan 900 na hukumar Inshorar Lafiya ta NHIS.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN ya ambato mai magana da yawon hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren na bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

Mista Uwujaren, ya yi zargin cewa kuɗin wani ɓangare ne da wasu bankunan ƙasar suka riƙe tun 2015 suka ƙi sanya wa a asusun hukumar Inshorar Lafiyar ƙasar wato NHIS.

Ya ƙara da cewa a yanzu an tura kuɗin zuwa asusun na NHIS.

Ya ci gaba da cewa a ranar 10 ga watan Fabrairun 2022, hukumarsu ta EFCC ta sakar wa NHIS ɗin naira biliyan 1.5 da ta kwato daga bankunan.

Haka kuma a ranar 5 ga watan Agustan 2022, EFCC ta ƙara sakar wa NHIS naira biliyan 1.4

A baya dai babban sakataren hukumar NHIS Farfesa Muhammad Nasir Sambo, ya sha yabawa da ƙwazon hukumar ta EFCC wajen taimaka wa NHIS ƙwato kuɗadenta da suka maƙale a wasu bankunan kasuwancin ƙasar.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp