fidelitybank

EFCC ta gano Naira miliyan 900 a hukumar NHIS

Date:

Hukumar Yaki da masu yi wa Tattalin Arzikin kasa ta’annati EFCC ta gano ƙarin naira miliyan 900 na hukumar Inshorar Lafiya ta NHIS.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN ya ambato mai magana da yawon hukumar ta EFCC Wilson Uwujaren na bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

Mista Uwujaren, ya yi zargin cewa kuɗin wani ɓangare ne da wasu bankunan ƙasar suka riƙe tun 2015 suka ƙi sanya wa a asusun hukumar Inshorar Lafiyar ƙasar wato NHIS.

Ya ƙara da cewa a yanzu an tura kuɗin zuwa asusun na NHIS.

Ya ci gaba da cewa a ranar 10 ga watan Fabrairun 2022, hukumarsu ta EFCC ta sakar wa NHIS ɗin naira biliyan 1.5 da ta kwato daga bankunan.

Haka kuma a ranar 5 ga watan Agustan 2022, EFCC ta ƙara sakar wa NHIS naira biliyan 1.4

A baya dai babban sakataren hukumar NHIS Farfesa Muhammad Nasir Sambo, ya sha yabawa da ƙwazon hukumar ta EFCC wajen taimaka wa NHIS ƙwato kuɗadenta da suka maƙale a wasu bankunan kasuwancin ƙasar.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp