fidelitybank

EFCC ta gaggauta bincikar mutanen da suka ci kuɗi wajen Akanta – HEDA

Date:

Ƙungiyar ci gaban bil’adama da muhalli (HEDA) ta rubutawa hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta’annati (EFCC) a cikin gaggawa ta fara gurfanar da duk wanda ke da hannu a badakalar naira biliyan 109 da aka yi a hannun Akanta-Janar na Tarayya, Idris Ahmed.

A cikin wata wasika mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar ta HEDA, Olanrewaju Suraju, da kuma aike wa shugaban hukumar EFCC, Mista Abdulrasheed Bawa, kungiyar yaki da cin hanci da rashawa, ta jaddada bukatar ta ne a kan fallasa da shaidan mai gabatar da kara na farko, Hayatudeen Ahmed, ma’aikacin EFCC ya yi. wanda ya binciki zargin da ake yi wa wadanda ake tuhuma.

Suraju ya ce Ahmed ya sanar da Kotun da sauran wasu alkaluma da suka kai Naira biliyan 94.39 a asusun bankin wanda ake kara na biyu.

Shugaban HEDA ya ce Ahmed ya shaida cewar wanda ake kara na biyu ya raba kudin ne tsakanin wani tsohon mataimakin gwamnan jihar Abia da kuma kwamishinan hukumar tattara kudaden shiga da kuma kasafin kudi (RMAFC) wanda aka ba shi Naira biliyan 18.8.

Suraju ya ce Ahmed ya kuma shaida cewa an baiwa kwamishinonin kudi na jihohi 9 da ake hako mai Naira biliyan 21.4 da dai sauransu.

Ya ce abin lura shi ne yadda aka mayar da kudaden zuwa dalar Amurka kafin a mika su ga wadanda suka amfana.

HEDA ta ce: “Muna kira ga EFCC da ta fara zurfafa bincike tare da gurfanar da dukkan kwamishinonin kudi na jihohi tara (9) na jihohi tara da ake hako mai a Najeriya da sauran masu hannu a badakalar naira biliyan 109 da kuma hada baki da akanta-janar da aka dakatar. na Tarayyar; Idris Ahmed.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp