fidelitybank

EFCC ta damƙe ƴan damfarar Yahoo Boys 18

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), ta kama wasu mutane 18 da ake zargi da damfarar yanar gizo, wadanda aka fi sani da “Yahoo boys” a unguwar Lekki da ke jihar Legas.

Kakakin hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Wilson Uwujaren, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, ya ce, an kama wadanda ake zargin ne, biyo bayan bayanan sirri da hukumar ta samu kan zarginsu da hannu wajen damfarar kwamfuta.

Sanarwar ta bayyana wadanda ake zargin sun hada da: Tijani Olumide Ahmed, Balogun Olusola, Ukuhor Richie Ifemeluona, Ologun Damilola, Adetokunbo Yusuf, Olubiyo Timilehin, Oyegoke Gafar Olaitan, Agarawu Faruq Okikiola, Kazeem Oluwadamilare Adebayo da kuma Salau Rahmon.

Sauran sun hada da: Abdulrahman Adeshina Olasunkanmi, Rasheed Remilekun, Adeyanju Kehinde Emmanuel, Owolabi Temidayo Habeeb, Ojora Usman Olawale, Mubarak Balogun, Rafiu Olusegun da Ayobami Habeeb Oyeleye.

Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin a cewar EFCC, sun hada da, motoci, kwamfutoci, wayoyin hannu da kuma layu.

Hukumar ta kuma bayyana cewa, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya bayan an kammala bincike.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp