fidelitybank

EFCC ta damƙe ƴan damfarar Yahoo Boys 18

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), ta kama wasu mutane 18 da ake zargi da damfarar yanar gizo, wadanda aka fi sani da “Yahoo boys” a unguwar Lekki da ke jihar Legas.

Kakakin hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Wilson Uwujaren, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, ya ce, an kama wadanda ake zargin ne, biyo bayan bayanan sirri da hukumar ta samu kan zarginsu da hannu wajen damfarar kwamfuta.

Sanarwar ta bayyana wadanda ake zargin sun hada da: Tijani Olumide Ahmed, Balogun Olusola, Ukuhor Richie Ifemeluona, Ologun Damilola, Adetokunbo Yusuf, Olubiyo Timilehin, Oyegoke Gafar Olaitan, Agarawu Faruq Okikiola, Kazeem Oluwadamilare Adebayo da kuma Salau Rahmon.

Sauran sun hada da: Abdulrahman Adeshina Olasunkanmi, Rasheed Remilekun, Adeyanju Kehinde Emmanuel, Owolabi Temidayo Habeeb, Ojora Usman Olawale, Mubarak Balogun, Rafiu Olusegun da Ayobami Habeeb Oyeleye.

Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin a cewar EFCC, sun hada da, motoci, kwamfutoci, wayoyin hannu da kuma layu.

Hukumar ta kuma bayyana cewa, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya bayan an kammala bincike.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp