fidelitybank

EFCC ta cafke mutane 9 a Abuja da zargin yin damfara a Intanert

Date:

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, ta kama wasu mutane tara da ake zargi da damfarar mutane ta yanar gizo a Abuja.

Wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai da wayar da kan jama’a, Wilson Uwujaren, ya fitar a ranar Laraba, ta ce an kama su ne a wani samame da aka kai musu.

Wadanda ake zargin dai su ne Bassey Sunday Junior, Samson Zakariah, Ogonyi Jeremiah, da Sunday Martins.

Sauran sun hada da Austin Yayison, Wilson Chinaza, Emmanuel Adeyi, Samuel Mark, da Emmanuel Bassey.

An kama su ne a ranar Talata, 30 ga watan Agusta a otal din Voque da ke Unguwar Mararaba a Abuja bisa zargin su da aikata laifuka ta yanar gizo.

An kwato wayoyi goma sha uku, kwamfutoci uku, da akwatin kida na Harman/Kardon daga hannunsu.

Hukumar EFCC ta bayyana cewa za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala bincike.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp