Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun kama wasu mutane bakwai da ake zargi da damfarar yanar gizo a babban birnin tarayya, FCT.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na Twitter ta ce an kama wadanda ake zargin ne a ranar 12 ga watan Agusta, 2020, a wani samame da suka kai a unguwar Tunlapal, Kurudu, Abuja.
An bayyana sunayensu da Nnonyelu Favor Chioma, Ajator Henry Sopulu, Ego Andy Seji, Okeke Ikechukwu Jude, Oshioriamite Perfect, da Ego Akin.
Abubuwan da aka kwato daga hannunsu sun hada da wayoyin hannu da na’urorin kwamfuta.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kara da cewa za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.