fidelitybank

EFCC ta cafke mai Siyar da ƙwayar ta intanet a Abuja

Date:

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta cafke MD/CEO na Marvelrock Pharmaceuticals and Stores Limited, Orakwe Chibuike Celestine.

An kama Celestine ne a babban birnin tarayya, bisa laifin yin cinikin haramtattun kwayoyi da sarrafa su a dandalin kasuwanci na intanet.

Wanda ya kammala karatun Business Administration a Jami’ar Abuja ya yi wa kamfanin harhada magunguna rajista a ranar 16 ga Disamba 2014.

An yi rajistar tare da takardar shaidar da goyon bayan wani mai lasisin magunguna, wanda ya fice daga yarjejeniyar a cikin 2017.

Amma wanda ake zargin ya ci gaba da gudanar da sana’ar tare da shigar da ita a dandalin yanar gizo a shekarar 2019, kamar yadda kakakin hukumar NDLEA, Femi Babafemi ya fitar a ranar Laraba.

An fara sa ido kan Celestine a watan Oktoba 2021 lokacin da ya tallata kayayyaki irin su Tramadol, allurar Ketamine Hydrochloride, Allunan Hypnox flunitrazepam, da sauransu, akan intanet.

Tsakanin 26 ga Oktoba 2021 zuwa 8 ga Agusta 2022, tawagar jami’an hana shan miyagun kwayoyi da aka sanya wa shari’ar sun tabbatar da cewa yana sayar da Tramadol 225mg da sauran magunguna ta yanar gizo.

“An kama wanda ake zargin dauke da wasu nau’ikan Tramadol da Swiphnol na Rohypnol a ranar Litinin 8 ga watan Agusta a wata mashaya da ke unguwar Jabi a Abuja inda ya je yin wasu kayayyaki.”

Shugaban hukumar ta NDLEA Mohamed Buba Marwa ya ce, bincike da kama dan kasuwar ya kamata su aike da sako mai karfi ga masu amfani da yanar gizo wajen siyar da miyagun kwayoyi da hukumar za ta samu.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp