Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC), ta kama Suleiman Gbajabiamila, wanda ake zargi da aikata laifuka biyu a gaban kotu, kan zargin sata da gabatar da kararrakin karya.
An kama Gbajabiamila ne a ranar Talata, 31 ga watan Janairu bisa zargin damfarar wani dan Najeriya dan kasar Birtaniya, Lateef Adeyemo kan kudi Naira miliyan 30.
An yi zargin cewa dan shekaru 63 da haihuwa ya gabatar da kansa a matsayin dillalin gidaje wani lokaci a shekarar 2021.
Karanta Wannan: NDLEA da EFCC sun yi babban kamu a Legas
Legit.ng ta tattaro cewa da wayo ya karbo kudi naira miliyan 30 da nufin ya samu daki biyu na Adeyemo dan kasar Birtaniya amma sai ya karkatar da kudin don amfanin kansa. An ruwaito lamarin ya faru ne tsakanin watan Satumba da Oktoban 2021.
An kama Gbajabiamila wanda aka ruwaito cewa, ya kwashe watanni da dama yana gudun hijira kuma an gurfanar da shi a gaban Alkalin Alkalai Adeola Olatunbosun. ‘Yan sanda sun gurfanar da shi a gaban kuliya inda suka bayyana cewa Gbajabiamila ya yi wasu hada-hadar kudade da akasari tsakaninsa da matarsa. Kamar yadda jaridar Guardian ta ruwaito, wanda ake zargin ya biya kudi Naira 150,000, domin bin diddigin Gbajabiamila wanda bai kunna wayarsa ba sai ranar Talata 20 ga watan Satumba, 2022. Nan take hukumomi suka bi sawun wanda ake zargin sannan suka kama shi.