fidelitybank

EFCC ta binciki asusun ƙananan hukumomin jihar Kano – APC

Date:

am’iyyar APC mai hamayya a jihar Kano, ta buƙaci hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta rufe asusun bankunan ƙananan hukumomin jihar 44.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin jihar suka ce sun fara gudanar da bincike kan zargin kwangilar sayen magani a ƙananan hukumomin, inda ake zargin an bai wa ɗan uwan jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Sanata Rabi’u Kwankwaso.

Cikin wata sanarwa da jam’iyar APC reshen jihar Kanon ta fitar mai ɗauke da sa-hannun shugabanta, Abdullahi Abbas, ta ce rufe asusun bankin ƙananan hukumomin ne kawai zai hana facaka da kuɗaɗen al’umma da sunan kwangila da kuma samun damar yin bincike.

Abdullahi Abbas ya ce ya kamata a gudanar da cikakken bincike kan badaƙalar da ake zargin an kashe maƙudan kuɗi wajen kwangilar samar da magunguna ga ƙananan hukumomin.

Sai dai a nata ɓangare jam’iyyar NNPP mai mulkin jihar, ta ce abin da APC ke yi barin jaki ne tana dukan taiki.

Shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Alhaji Hashim Dungurawa ya ce kamata ya yi jam’iyyar APC ta ce a binciki Ganduje kan zargin sayar da wasu filaye a jihar, da sauran laifukan da ake zargin gwamnatin APC da ta gabata a jihar ta aikata.

Ya ƙara da cewa ai abin da EFCC take yi shi ne abinda hukumar yaƙi da rashawa ta jihar ke yi, ”duk hukumomi ne da ke aiki bisa tsarin dokar”, kamar yadda ya shaida wa BBC.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da karɓar korafe-korafe ta jihar Kano, ta ce ta gayyaci ɗan’uwan jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa Rabi’u Musa Kwankwaso, wato Musa Garba Kwankwaso wanda shi ne ake zargin an saka kuɗaɗen kwangilar sayen maganin a asusun bankin kamfaninsa.

Shugaban hukumar Barista Muhuyi Magaji Rimi Gado ya ce cikin waɗanda hukumarsa ta gayyatar har da babban sakatare a ma’aikatar ƙananan hukumomi da wasu daraktoci, kuma bayan bincikarsu sun ce su tafi za su zake nemansu nan gaba.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp