fidelitybank

EFCC ta bankado Dala miliyan 72.8 a asusun tsohuwar Minista

Date:

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC), ta sake bankado Dalar Amurka miliyan 72.8 a wani asusun ajiyar kudi na tsohuwar Ministar Albarkatun Mai, Diezani Alison-Madueke.

EFCC ta ce ta gano kudaden ne a asusun Diezanni da bankin Fidelity a Najeriya.

Bayan haka kuma hukumar ta cafke tsohon daraktan bankin mai suna, Nnamdi Okonkwo, wanda a yanzu na daya daga shugabannin bankin ‘First Bank’ wanda a baya ya sha tambayoyi kan Dala miliyan 153 da kuma Dala miliyan 115.

Duk da cewa EFCC ta karbi Dala miliyan 153, har yanzu batun Dala miliyan 115 da a ke zargin shi a kansu na gaban kotu. Inji Aminiya.

A yanzu dai Mista Okonkwo da Charles Onyedibe na hannun EFCC inda suke amsa tambayoyi kan Dala miliyan 72.8 da aka samu a asusun Diezani.

Ko a watannin da suka gabata sai da gwamnatin tarayya ta yi gwanjon wasu kadarorin da ta gano daga Diezani.

Tun bayan saukar ta daga kujerar minista, Diezani ke shan tuhume-tuhume kan zargin badakala da dukiyar kasa.

 

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp