Hukumar yaƙi da rashawa ta Najeriya (EFCC) ta ce ta kama mutum 25 waɗanda take zargin masu damfara ne ta intanet a wani wuri da ake kyautata zaton wurin horas da damfara ne, a birnin Benin na jihar Edo.
Cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na X, EFCC ta ce ta samu nasarar yin hakan ne a ranar Alhamis ta hanyar amfani da jami’anta na shiyyar Benin.
Bayanin ya ƙara da cewa “kamen ya biyo bayan sahihan bayanan sirri ne da ta tattara, waɗanda ke nuna cewa ana amfani da wani gini a matsayin wurin koyar da damfarar yahoo ko kuma horas da masu son ƙwarewa a sauran hanyoyin damfara ta intanet.
Hukumar ta ce ta kuma gano wasu kaya a lokacin samamen nata, waɗanda suka haɗa da dalla-dallan motoci guda shida, da kwamfutoci da kuma wayoyi.
Najeriya dai ta yi ƙaurin suna a harkar damfara ta intanet a duniya.