fidelitybank

EFCC ta ƙwace unguwar da wani tsohon jami’in gwamnati ya mallaka a Abuja

Date:

Hukumar EFCC ta samu nasarar ƙwace kadara mafi girma a tarihinta, inda a ranar Litinin, 2 ga watan Disamban 2024, mai shari’a Jude Onwuegbuzie ya mallaka wa gwamnati wani rukunin gidaje, wanda aka gina a fili mai mai faɗin murabba’in ƙasa 150,500, mai ɗauke da rukunin gidaje 753 da wasu gine-ginen a Abuja.

Wannan shi ne ƙwace kadara mafi girma tun bayan kafa hukumar EFCC a shekarar 2003.

Kotu ta ƙwace rukunin gidajen ne mai lamba 109 a yankin Zone C09 da ke unguwar Lokogoma a Abuja, wanda kotun ta ce ta mallakin wani tsohon jami’in gwamnati ne, kamar yadda wata sanarwa da EFCC ta fitar ta nuna.

Da yake hukunci kan ƙwace rukunin gidajen, mai sharii’a Onwuegbuzie ya ce wanda ake ƙara ya kasa gamsar da kotun abin da zai hana a ƙwace masa kadarar, “wadda ake zargin ya mallaka da kuɗaɗen da ya samu ta wasu hanyoyi zamba. Don haka an ƙwace kadarar, an kuma miƙa ga gwamnatin tarayya.”

Tun da farko, a ranar 1 ga watan Nuwamban 2024 ne kotun ta fara ƙwace rukunin gidajen na wucin-gadi, kafin yanzu ta ƙwace baki ɗaya.

Sanarwar ta ƙara da cewa ana cigaba da binciken jami’in gwamnatin

Shugaban hukumar, Mr Ola Olukoyede, ya sha nanata cewa ƙwace kadarorin da aka mallaka ta hanyoyi marasa kyau na da matuƙar muhimmanci a yaƙi da cin hanci da rashawa.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp