fidelitybank

EFCC ta ƙara gurfanar da Emefiele a kan sababbin kuɗin Naira da ya buga

Date:

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa arziki ta’annati, EFCC za ta gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin ƙasar Godwin Emefiele ranar Laraba saboda ba da izinin buga sabbin takardun naira na miliyan 684.5 a kan naira biliyan 18.96.

Tun farko an tsara gurfanar da shi ne ranar 30 ga watan Afrilu da ya gabata amma aka ɗage ranar bayan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kotun da kuma ɓangarorin.

A tuhume-tuhumen huɗu da aka shigar a kansa, EFCC ta yi zargin Emefiele ya yi burus da umarnin kotu da nufin jefa jama’a cikin mawuyacin hali lokacin aiwatar da tsarin sauya takardun naira da gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi.

EFCC ta kuma zargi Emefiele da ba da izinin cirar naira biliyan 124.9 daga asusun bai ɗaya na ajiyar kuɗaɗen shu=iga na gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa tsohon gwamnan CBN zai gurfana a gaban kotu kan waɗannan tuhume-tuhume gaban mai shari’a Maryann Anenih ta babbar kotun tarayya da ke Abuja.

A ranar 17 ga watan Nuwamban 2023, an gurfanar da Emefiele gaban mai shari’a Hamza Muazu kan tuhume-tuhume shida kan wata badaƙala ta siyan kayayyaki, zargin da ya musanta.

An kuma zarge shi da yin amfani da matsayinsa wajen amincewa da kwangilar siyan motoci 43 a kan kuɗi naira biliyan 1.2 daga 2018 zuwa 2020.

A cikin 8 ga watan Afrilun 2014 ne kuma EFCC ta sake gurfanar da Emefiele tare da Hnery Omoile gaban mai shari’a Rahman Oshodi na kotun sauraron laifuka na musamman da ke zamanta a Ikeja, jihar Legas kan zargin badaƙalar kuɗi ta dala biliyan 4.5 da kuma naira biliyan 2.8.

Emefiele dai ya musanta yin badaƙalar.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp