fidelitybank

EFCC sun gayyaci dan takarar gwamnan jihar Ondo a jam’iyyar APC

Date:

Wani dan takarar gwamna a jam’iyyar All Progressives Congress, APC a jihar Ondo, Wale Akinterinwa, ya ce zai mutunta gayyatar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC ta yi masa ranar Alhamis.

Akinterinwa wanda ya fafata da wasu mutane 15 na tikitin takarar gwamnan jam’iyyar a ranar Asabar din da ta gabata, hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta gayyaci Akinterinwa bisa zargin karkatar da kudade.

A baya dai rahotanni sun nuna cewa hukumar EFCC na binciken Akinterinwa bisa zargin karkatar da biliyoyin Naira a lokacin da yake rike da mukamin kwamishinan kudi a lokacin gwamnatin marigayi Rotimi Akeredolu.

Rahoton ya yi zargin cewa EFCC ta gayyace shi ne makonnin da suka gabata don tattaunawa kan wasu zarge-zarge amma ya “yi matukar shakku” don girmama gayyatar.

Sai dai a wani sako da ya fitar a shafinsa na X da aka tabbatar a ranar Alhamis, ya ce, “A yau, zan girmama gayyatar da hukumar EFCC ta yi min domin yin karin haske kan wasu batutuwa da hukumar ke son yin karin haske a kai.

“Ina da kwarin gwiwa ga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta gudanar da cikakken bincike tare da tabbatar da cewa an yi adalci”.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp