Babbar kotun tarayya da ke zaman ta a garin Abuja, ta yanke hukunci cewa, a raba Rochas Anayo Okorocha da wasu gidajensa da su ke birnin Abuja.
Mai magana da yawun bakin EFCC na kasa, Wilson Uwujaren ya bayyana cewa, su na zargin da dukiyar haram Rochas Okorocha ya mallaki wannan gidan.
Kamar yadda hukumar ta bayyana, za a raba tsohon gwamnan na jihar Imo da wannan kadara ne har zuwa lokacin da za a kammala shari’ar da ake yi da shi.
Gidan talabijin na Channels rawaito cewa, Alkali Emeka Nwite ya zartar da wannan hukunci a zaman da ya yi a ranar Alhamis, 24 ga watan Fubrairu 2022.