fidelitybank

EFCC ba ta kama ni ba – Mele Kyari

Date:

Tsohon hugaban kamfanin mai na NNPCL, Mele Kyari, ya musanta rahotanni da ke cewa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta kama shi – kan wani bincike da ake yi na zargin almundahanar kuɗi da ya kai dala biliyan 2.9, wanda aka ware don sake gyara matatun ƙasar.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Asabar, Kyari ya yi watsi da rahotannin – inda ya ce wasu ne kawai ke son ɓata masa suna.

“A tsawon kwanaki da suka gabata, na samu kiraye-kiraye daga ƴan uwa da abokai kan rahoton da wata jarida ta yaɗa cewa ina tsare a ofishin EFCC.

“Wannan kawai yunkuri ne na ɓata min suna da jaridar da kuma waɗanda suka ɗauki nauyinta ke son yi,” in ji Kyari.

Ya kuma ce a shirye yake wajen faɗar gaskiyar abin da ya gudanar a ofishinsa lokacin da yake shugabancin NNPCL.

“Zan ƙara nanata cewa na riƙe mukamin da aka bisa tsoron Allah, domin ko ban faɗi gaskiya a nan ba, zan faɗa a gaban Allah, in ji shi.

A farkon watan Afrilu ne, shugaba Bola Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin kamfanin mai na ƙasar NNPCL, inda ya maye gurbinsa da Injiniya Bashir Bayo Ojulari.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp