Tsohon hugaban kamfanin mai na NNPCL, Mele Kyari, ya musanta rahotanni da ke cewa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta kama shi – kan wani bincike da ake yi na zargin almundahanar kuɗi da ya kai dala biliyan 2.9, wanda aka ware don sake gyara matatun ƙasar.
A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Asabar, Kyari ya yi watsi da rahotannin – inda ya ce wasu ne kawai ke son ɓata masa suna.
“A tsawon kwanaki da suka gabata, na samu kiraye-kiraye daga ƴan uwa da abokai kan rahoton da wata jarida ta yaɗa cewa ina tsare a ofishin EFCC.
“Wannan kawai yunkuri ne na ɓata min suna da jaridar da kuma waɗanda suka ɗauki nauyinta ke son yi,” in ji Kyari.
Ya kuma ce a shirye yake wajen faɗar gaskiyar abin da ya gudanar a ofishinsa lokacin da yake shugabancin NNPCL.
“Zan ƙara nanata cewa na riƙe mukamin da aka bisa tsoron Allah, domin ko ban faɗi gaskiya a nan ba, zan faɗa a gaban Allah, in ji shi.
A farkon watan Afrilu ne, shugaba Bola Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin kamfanin mai na ƙasar NNPCL, inda ya maye gurbinsa da Injiniya Bashir Bayo Ojulari.