fidelitybank

EFCC ta kama ƴan Yahoo 23 a Sokoto

Date:

Jami’an hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa ta (EFCC), sun kama wasu matasa 23 bisa zargin zambatar mutane ta intanet da aka fi sani da ‘Yahoo” a jihar Sokoto.

Gidan Talbijin na ƙasar NTA ya ambato mai magana da yawun hukumar reshen jihar Sokoto Kamal Ibrahim na cewa sun kama mutanen bayan samun bayan sirri kan ayyukan da suke aikata.

EFCCn ta ce jami’anta sun riƙa lura da bin sawun harkokokin matasan, inda suka gano suna rayuwa fiye da abin da yakamata ace suna samu a sana’o’in da suke iƙirarin gudanarwa.

An dai kama matasan ne da maraicen ranar Juma’a a rukunin gidajen Bafarawa da ke garin Sokoto da rukunin gidajen Kalkalawa da ke yankin Kalkalawa a jihar, inda a yanzu suka hannun hukumar domin ci gaba da gudanar da bincike.

Abubuwan da aka kama matasan da su, sun haɗar da ƙananan kotoci guda biyu da kwamfutoci da injin bayar da hasken lantarki da mayan wayoyin hannu 30.

Hukumar ta ce za ta gabatar da su a gaban kotu da zarar ta kammala gudanar da bincike a kansu.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp