fidelitybank

ECOWAS za su gana Ghana akan yadda za su yaƙi Nijar

Date:

Manyan hafsoshin sojin Afirka ta Yamma ECOWAS, za su gudanar da taro a ‘yan kwanaki masu zuwa don tsara shirye-shirye kan yiwuwar amfani da ƙarfin soja, yayin da ƙasashen duniya ke ƙara nuna fargaba game da yanayin da ake tsare da hamɓararren Shugaba Bazoum Mohamed.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce taron manyan hafsoshin sojin na nuna cewa ƙasashen Afirka ta Yamma suna gaggauta shirye-shiryen tura sojoji da yiwuwar ɗaukar matakin kawar da masu juyin mulki a Nijar.

“Ana tsara yin wani (taron) a makon gobe,” Reuters ya ambato wani mai magana da yawun Ecowas yana cewa.

Wani jami’in gwamnatin Najeriya da kuma wata majiyar sojojin Kwatdebuwa sun ce za a yi taron ne ranar Asabar a Ghana.

Zuwa yanzu babu masaniya ƙarara kan yadda girman rundunar zai kasance, da tsawon lokacin da za a shafe kafin a iya tattaro dakarun, da kuma idan haƙiƙa rundunar za ta auka don yin mamaye.

Ƙungiyar Ecowas dai ta ce har yanzu duk ƙofofi a buɗe suke kuma tana fatan za a iya cimma masalaha cikin lumana. Masu sharhi kan al’amuran tsaro kuma sun ce dakarun Ecowas na iya kwashe tsawon makonni ko fiye da haka, kafin su haɗu, abin da mai yiwuwa zai ba da dama ga ƙoƙarin tattaunawa.

Kwatdebuwa ce kaɗai ƙasar da ya zuwa yanzu ta bayyana adadin dakarun da za ta aika. Shugaba Alassane Ouattara ya yi alƙawari a ranar Alhamis cewa ƙasarsa za ta aika wata bataliyar sojoji da ta kai yawan mutum 850 – 1,100. In ji BBC.

Hamɓarar da gwamnatin Mohamed Bazoum ya kasance juyin mulki na bakwai a Yammaci da Tsakiyar Afirka cikin shekara uku, abin da kuma ya ƙara jefa yankin cikin tunzuri, baya ga hare-haren masu iƙirarin jihadi da yake fama da su tsawon lokaci

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp