Shugabannin ƙasashe mambobin Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika wato ECOWAS na gudanar da taro a ranar Laraban nan a Najeriya domin bikin cikar ƙungiyar shekara 50 da kafuwa.
Shugabanni da jami’an gwamnati daga ƙasashe 12 na Yammacin Afrika ne suke halartar bikin da ake gudanarwa a birnin Lagos, ƙarkashin jagorancin shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.
Wannan bikin na zuwa ne a daidai lokacin da ake tambaya kan makomar ƙungiyar ECOWAS ɗin bayan ficewar wasu ƙasashen yankin Sahel da sojoji ke mulki sakamakon juyin mulki da suka yi.