Shugabannin ƙasashen Yammacin Afirka za su gudanar da taro a Najeriya yau Lahadi, yayin da wasu ƙasashen yankin ke fama da rikicin siyasa.
Taron nasu na zuwa ne kwana guda bayan ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka sanar da yanke hulda da ƙungiyar Ecowas.
Ana sa ran batun ficewar ƙasashen uku daga ƙungiyar da kuma kafa runduna tsaro ta musamman don yaƙi da matsalar tsaro da yankin ke fuskanta ne za su kankane taron na Ecowas da za a yi a Abuja fadar gwamnatin jihar.
Wasu daga cikin shugabannin ƙasashen yankin ne dai suka kira taron na yau da nufin sasantawa da jagororin mulkin sojin ƙasashen uku.
A taron da shugabannin Mali da Nijar da Burkina Faso suka gudanar jiya a birnin Yamai, Shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, ya ce ƙasashen uku ba za su koma cikin ƙungiyar Ecowas ba, bayan da suka zargi ƙungiyar da haɗa kai da Faransa.
Sojojin mulkin ƙasashen sun kori dakarun Faransa daga ƙasashensu, sannan suka koma ƙulla ƙawance da Rasha.
Amurka ce ƙasa ta baya-bayan nan daga ƙasashen Yamma da za ta janye dakarunta daga Nijar, bayan da ƙasar ta soke yarjejeniyar ƙawance sojinta da Amurka.


