fidelitybank

ECOWAS na gudanar da taro a Abuja

Date:

Shugabannin ƙasashen Yammacin Afirka za su gudanar da taro a Najeriya yau Lahadi, yayin da wasu ƙasashen yankin ke fama da rikicin siyasa.

Taron nasu na zuwa ne kwana guda bayan ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka sanar da yanke hulda da ƙungiyar Ecowas.

Ana sa ran batun ficewar ƙasashen uku daga ƙungiyar da kuma kafa runduna tsaro ta musamman don yaƙi da matsalar tsaro da yankin ke fuskanta ne za su kankane taron na Ecowas da za a yi a Abuja fadar gwamnatin jihar.

Wasu daga cikin shugabannin ƙasashen yankin ne dai suka kira taron na yau da nufin sasantawa da jagororin mulkin sojin ƙasashen uku.

A taron da shugabannin Mali da Nijar da Burkina Faso suka gudanar jiya a birnin Yamai, Shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, ya ce ƙasashen uku ba za su koma cikin ƙungiyar Ecowas ba, bayan da suka zargi ƙungiyar da haɗa kai da Faransa.

Sojojin mulkin ƙasashen sun kori dakarun Faransa daga ƙasashensu, sannan suka koma ƙulla ƙawance da Rasha.

Amurka ce ƙasa ta baya-bayan nan daga ƙasashen Yamma da za ta janye dakarunta daga Nijar, bayan da ƙasar ta soke yarjejeniyar ƙawance sojinta da Amurka.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp