fidelitybank

ECOWAS na gudanar da babban taron ta a Abuja

Date:

Yau Asabar ne kuma Shugabannin ƙasashen ƙungiyar ECOWAS ko CEDEO za su gudanar da taro a Abuja babban birnin Najeriya.

Yankin na yammacin Afrika na fuskantar barazanar rashin haɗin kai tun bayan da ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar suka bayyana aniyarsu ta ficewa daga ƙungiyar.

Yayin da a ɗayan ɓangaren ƙasar Senegal ke fama da dambarwar siyasa sakamakon matakin shugaba Macky Sall na ɗage babban zaɓen ƙasar.

Ana saran dai a wanann taro ƙungiyar za ta lalubo mafita kan wadanan matsaloli da suka mamaye yankin.

Wannan zai iya zama gagarumin ƙalubale da kungiyar ke fuskanta tun bayan kafata shekaru 50 da suka gabata.

Hudu cikin mambobin ƙungiyar 15 yanzu haka na ƙarƙashin shugabancin soji.

Taron kuma na zuwa ne bayan da tsohon shugaban Najeriya na mulkin soja, kuma shugaba ɗaya tilo da ya rage cikin waɗanda suka kafa ƙungiyar ta ECOWAS ko CEDEO, Janar Yakubu Gowon mai ritaya, ya yi kira da a gaggauta ɗage duk wani takunkumin da aka ƙaƙaba wa ƙasashen Gini da Burkina Faso da Mali da kuma Nijar.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp