Gwamna jihar Ebonyi, David Umahi ya tabbatar da cewa, jiharsa ba za ta taɓa shiga yunƙurin kafa ƙasar Biafra ba.
Umahi wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin Najeriya a jam’iyyar APC mai mulki, ya faɗi hakan ne a Abakaliki babban birnin jihar ranar Alhamis yayin wata liyafa da aka haɗa masa.
Kazalika gwamnan ya roƙi hukumomin Najeriya da su murƙushe duk wanda ke son tayar da hankali a yankinsu na kudu maso gabas.
Ya ce, “Abu na farko dai, na sha faɗa, duk wanda ya tambaye ku game da Biafra ku ce Ebonyi ba za ta taɓa shiga Biafra ba. Mu ba ‘yan Biafra ba ne.An wulaƙanta mu a baya kuma yanzu ne muke wartsakewa, amma kuna so mu koma baya. Ba za mu koma ba.
“Na faɗa wa gwamnonin yankin Kudu maso Gabas cewa, mu muna son mafita ne ta hanyar siyasa, sannan kuma duk wanda ya ke son tayar da hankali a murƙushe shi.Babu wani ɗan ƙabilar Igbo da zai zama shugaban ƙasa kuma ba zai so ɗorewar Najeriya a matsayin ƙasa ɗaya ba, saboda muna da dukiya a ko’ina a faɗin Najeriya”. A cewar Umahi.