fidelitybank

Ebonyi ba za ta taba shiga tsagin Biafara ba – Umahi

Date:

Gwamna jihar Ebonyi, David Umahi ya tabbatar da cewa, jiharsa ba za ta taɓa shiga yunƙurin kafa ƙasar Biafra ba.

Umahi wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin Najeriya a jam’iyyar APC mai mulki, ya faɗi hakan ne a Abakaliki babban birnin jihar ranar Alhamis yayin wata liyafa da aka haɗa masa.

Kazalika gwamnan ya roƙi hukumomin Najeriya da su murƙushe duk wanda ke son tayar da hankali a yankinsu na kudu maso gabas.

Ya ce, “Abu na farko dai, na sha faɗa, duk wanda ya tambaye ku game da Biafra ku ce Ebonyi ba za ta taɓa shiga Biafra ba. Mu ba ‘yan Biafra ba ne.An wulaƙanta mu a baya kuma yanzu ne muke wartsakewa, amma kuna so mu koma baya. Ba za mu koma ba.

“Na faɗa wa gwamnonin yankin Kudu maso Gabas cewa, mu muna son mafita ne ta hanyar siyasa, sannan kuma duk wanda ya ke son tayar da hankali a murƙushe shi.Babu wani ɗan ƙabilar Igbo da zai zama shugaban ƙasa kuma ba zai so ɗorewar Najeriya a matsayin ƙasa ɗaya ba, saboda muna da dukiya a ko’ina a faɗin Najeriya”. A cewar Umahi.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp