fidelitybank

Dusar Kankara ya sanya an dakatar da wasan Banyern Munich

Date:

An dage karawar da Bayern Munich za ta yi da Union Berlin, saboda ruwan dusar kankara a babban birnin Bavaria, kamar yadda hukumomi suka tabbatar a ranar Asabar.

An shirya gudanar da wasan ne a ranar Asabar da yamma amma sanarwar manema labarai daga Bayern ta ce “hatsarin tsaro da yanayin zirga-zirga ya sanya ba a iya kaucewa.”

Karancin yanayin zafi ya haifar da dusar ƙanƙara a kudancin Jamus, musamman a Munich.

Gabanin soke wasan dai tuni hukumomin sufuri na birnin Munich suka dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a yankin mafi girma na Munich, yayin da cunkoson ababen hawa suka tsaya cak.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, Bayern ta ce akwai “hadari mara misaltuwa ga ‘yan kallo” kuma ta bayyana “ba shi yiwuwa a isa filin wasa na Arena”.

“A karkashin waÉ—annan sharuÉ—É—an, ba za a iya ba da tabbacin cewa jami’an tsaro da sauran ma’aikatan filin wasan da suka dace don ci gaba da wasan za su iya zuwa filin wasa na Allianz.”

Shugaban Bayern Jan-Christian Dreesen ya ce “Mun yi nadama sosai cewa muna bukatar soke wasan, amma amincin magoya bayanmu da masu goyon bayan Union Berlin shi ne cikakken fifiko,” in ji shugaban Bayern Jan-Christian Dreesen a cikin wata sanarwa.

Hukumar kula da kwallon kafa ta Jamus (DFL) da ke gudanar da gasar Bundesliga ta tabbatar da soke wasannin a ranar Asabar kuma ta ce nan ba da jimawa ba za a sanar da sabon ranar da za a buga wasan.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp