Dusar kankarar ce ke sauka yanzu a saudiya. Dusar kankarar ta mamaye duwatsun Al-Lawz dake yankin Tabuk, tun ranar Talata, a cewar kamanin dillancin labaran Saudiya SPA.
Wuraren da kankarar ke zuba ya zama abun jan hankalin ga mazuna yankin da baki ‘yan yawon bude idanu, da suka zo daga kasashe don shakatawa acikin dusar dake zuba.
Daraktan hukumar kula da yanayi a birnin Alenizi da ke arewacin Saudiya ya ce zubar dusar kankarar na baya rasa nasaba da dalilai guda biyu, a duwatsun Al-Lawz da sauran wasu yankuna da ke kusa da shi.