Shugaban Ukraine Zelensky ya yi gagardi cewa, rikicin da ake yi a kasar zai iya haddasa matsalar karancin abinci a duniya.
Da yake magana da wani shirin labarai na Australia mai taken 60 Minutes, Zelensky ya ce kasarsa za ta yin asarar miliyoyin tan na hatsi saboda Rasha ta rufe tashar jiragen ruwa da ke isa Bahar Aswad.
Ukraine na daya daga cikin kasashen duniya da ke fitar da hatsi da sauran kayan abinci.
“Rasha tana ta durkusar da tattalin arzikin kasarmu baki daya,” Zelensky.