Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya yi kira ga kasashen duniya su taimaka wa sojojin Jamhuriyar Nijar, domin yaki da masu tayar da kayar baya da suke yawan kai hare-hare a kasar.
A yayin da jawabi lokacin wata ziyara da ya kai Niamey, babban birnin kasar, babban jami’in na Majalisar Dinkin Duniya ya ce rikicin da ke faruwa a yankin Sahel ya zama babbar barazana ga duniya.
Antonio Guterres ya kara da cewa, Jamhuriyar Nijar ba za ta iya tunkarar matsalar masu ikirarin jihadi ita kadai ba, kuma ya yi kira ga wasu kasashe su taimaka mata da horaswa da kuma kayan yaki.
Faransa da Amurka suna da sansanonin soja a Jamhuriyar Nijar.
Jamhuriyar Nijar mamba ce, ta kasashen G5 Sahel da ke yaki da masu tayar da kayar-baya da suka hada da Mauritania, Mali, Burkina Faso da kuma Chadi. A cewar BBC.