An gurfanar da wani tela mazaunin Kaduna, Gado Yahaya a gaban kotun majistare a ranar Litinin kan zarginsa da kashe makwabincinsa yayin rikici a kan bokitin ruwa a Kaduna.
Yahaya ya shaida wa kotun majistaren cewa, shekarunsa 29, kuma ya na cike da nadama a kotun, kamar yadda Vanguard ta rawaito.
Rikici game da bokitin ruwa ya faru ne a unguwar Rigasa Kaduna, kamar yadda ganau ya shaidaw, Alkalin kotun majistare a Kaduna.
Mai gabatar da karar, Sifeta Chidi Leo ya yi ikirarin cewa,“Yahaya ya kashe Salisu da tabarya ne yayin da suke fada kan bokitin ruwa. “A yayin fadan, ya shiga dakin girki, ya dauko tabarya ya buga wa Salisu a kai, nan ya yanke jiki ya fadi bayan buga masa tabaryar a kai, ya mutu a hanyar mu na zuwa asibiti.” A cewar Mr Leo, Mai gabatar da karar.
Sai dai Yahaya ya rubuta cewa, ya aikata hakan ya kuma saka hannu a lokacin da aka kawo shi ofishin ‘yan sanda domin masa tambayoyi.