Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin janye jami’an ‘yan sandan da aka tura a baya domin rufe kananan hukumomi 23 na jihar Ribas.
An sanar da wannan umarnin ne a ranar Litinin a wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, Grace Iringe-Koko ta fitar.
Sanarwar ta ce, umarnin ya biyo bayan ci gaban siyasa da aka samu a jihar Ribas.
“Sabon kwamishinan ‘yan sandan jihar, Bala Mustapha, ya mika umarnin babban sufeton ‘yan sanda na kasa, IGP Kayode Egbetokun, na gaggauta janye dukkan jami’an ‘yan sandan da aka tura a baya domin rufewa da kuma kare sakatarorin kananan hukumomin jihar.”
Sanarwar ta jaddada cewa matakin “ya yi daidai da kudurin rundunar ‘yan sandan Najeriya na tabbatar da tsaka-tsaki da kuma gudanar da ayyukan dimokuradiyya cikin sauki.
Ya kuma kara da cewa za a sake tura ma’aikata zuwa yankunan ne kawai idan aka samu rikici ko kuma tabarbarewar doka da oda, inda a nan ne za a gaggauta aiwatar da matakan gaggawa domin dawo da zaman lafiya.
Rundunar ‘yan sandan jihar Ribas ta bai wa al’umma tabbacin ci gaba da jajircewarta wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin jihar, yayin da ta kuma jaddada kwazonta wajen gudanar da ayyukanta.
An yi kira ga jama’a da masu ruwa da tsaki da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka da oda yayin da lamarin ke faruwa.