fidelitybank

Dukkannin jami’an mu su janye daga ƙananan hukumomin Ribas – Rundunar Ƴansanda

Date:

Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin janye jami’an ‘yan sandan da aka tura a baya domin rufe kananan hukumomi 23 na jihar Ribas.

An sanar da wannan umarnin ne a ranar Litinin a wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, Grace Iringe-Koko ta fitar.

Sanarwar ta ce, umarnin ya biyo bayan ci gaban siyasa da aka samu a jihar Ribas.

“Sabon kwamishinan ‘yan sandan jihar, Bala Mustapha, ya mika umarnin babban sufeton ‘yan sanda na kasa, IGP Kayode Egbetokun, na gaggauta janye dukkan jami’an ‘yan sandan da aka tura a baya domin rufewa da kuma kare sakatarorin kananan hukumomin jihar.”

Sanarwar ta jaddada cewa matakin “ya yi daidai da kudurin rundunar ‘yan sandan Najeriya na tabbatar da tsaka-tsaki da kuma gudanar da ayyukan dimokuradiyya cikin sauki.

Ya kuma kara da cewa za a sake tura ma’aikata zuwa yankunan ne kawai idan aka samu rikici ko kuma tabarbarewar doka da oda, inda a nan ne za a gaggauta aiwatar da matakan gaggawa domin dawo da zaman lafiya.

Rundunar ‘yan sandan jihar Ribas ta bai wa al’umma tabbacin ci gaba da jajircewarta wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin jihar, yayin da ta kuma jaddada kwazonta wajen gudanar da ayyukanta.

An yi kira ga jama’a da masu ruwa da tsaki da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka da oda yayin da lamarin ke faruwa.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp