fidelitybank

Duk wata hadakar jam’iyyun adawa ba za ta hana Tinubu yin tazarce ba – Ganduje

Date:

Shugaban Jam’iyyar APC mai mulki, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce duk wata haɗaka da jam’iyyun hamayyar ƙasar nan ke shirin yi da nufin kawar da APC a zaɓen 2027 ba za ta yi tasiri ba.

Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi ga manema labarai a jihar Kaduna lokacin ziyarar – da ya jagoranci shugabannin jam’iyyar wajen kai wa tsohon shugaban ƙasar – Muhammadu Buhari.

Gabanin ziyarar su Gandujen, tawagar jagoran adawar ƙasar, Atiku Abubakar tare da tsoffin gwamnonin jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai da Sanata Ahmed Makarfi da kuma Sanata Aminu Waziri Tambuwal ta fara kai wa Buhari ziyara a gidan nasa.

Ganduje ya ce ziyarar su Atikun ba ta ɗaga musu hankali ba, saboda a cewarsa ”suna son ƙulla wata haɗaka da ba za ta yi tasiri ba”.

”Daga abin da muka gani mutane ne da ba za su iya haɗuwa ƙarƙashin inuwa guda ba”, in ji shi.

Shugaban jam’iyyar ta APC ya ce a shirye suke kuma sun san yadda za su ɓullo wa lamarin kodayake ya ce ba zai faɗi dabarar da za su bi ba.

Ganduke ya ce duk da cewa a yanzu haka APC na da iko da jihohin ƙasar 21, har yanzu jam’iyyarsu na hangen ƙarin wasu jihohin.

”Ko dai wasu gwamnonin da kansu su dawo jam’iyyarmu, ko kuma jihohin su dawo hannunmu ta hanyar zaɓe.”

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp