fidelitybank

Duk wanda zai shigo Najeriya ba sai an yi masa gwajin Korona ba – Boss Mustapha

Date:

Gwamnatin Najeriya ta ce,, sabbin dokokin yaƙi da annobar korona da ta sauƙaƙa wa matafiya za su fara aiki ne daga gobe Litinin, a cewar shugaban kwamatin yaƙi da korona na shugaban ƙasa Boss Mustapha.

Sabbin dokokin da kwamatin ya fitar sun ƙunshi cewa, duk wanda ke son shiga Najeriya ba sai ya yi gwajin cutar na shigowa ba da kuma bayan sauka matuƙar dai an yi masa rigakafin cutar.

Su ma yara ‘yan ƙasa da shekara 18 za su samu wannan alfarmar ko da ba a yi musu rigakafin cutar ba.

Sai dai kuma, masu son shiga ƙasar da ba a yi wa rigakafin ba, ko kuma ba su samu cikakkiya ba, har yanzu dole ne sai sun yi gwaji kwana biyu kafin su shiga sannan kuma su yi na bayan sauka, da kuɗinsu.

A gefe guda kuma, dukkan fasinjojin da ke son zuwa Najeriya sai sun yi rajista a shafin matafiya na gwamnati a adireshin NITP– https://nitp.ncdc.gov.ng.

‘Yan Najeriyar da ke son zuwa ƙasashen waje kuwa, an shawarce su da su yi rigakafin sannan kuma su san dokokin ƙasashen da za su je na yaƙi da korona kafin su tafi.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp