Gwamnatin Najeriya ta ce,, sabbin dokokin yaƙi da annobar korona da ta sauƙaƙa wa matafiya za su fara aiki ne daga gobe Litinin, a cewar shugaban kwamatin yaƙi da korona na shugaban ƙasa Boss Mustapha.
Sabbin dokokin da kwamatin ya fitar sun ƙunshi cewa, duk wanda ke son shiga Najeriya ba sai ya yi gwajin cutar na shigowa ba da kuma bayan sauka matuƙar dai an yi masa rigakafin cutar.
Su ma yara ‘yan ƙasa da shekara 18 za su samu wannan alfarmar ko da ba a yi musu rigakafin cutar ba.
Sai dai kuma, masu son shiga ƙasar da ba a yi wa rigakafin ba, ko kuma ba su samu cikakkiya ba, har yanzu dole ne sai sun yi gwaji kwana biyu kafin su shiga sannan kuma su yi na bayan sauka, da kuɗinsu.
A gefe guda kuma, dukkan fasinjojin da ke son zuwa Najeriya sai sun yi rajista a shafin matafiya na gwamnati a adireshin NITP– https://nitp.ncdc.gov.ng.
‘Yan Najeriyar da ke son zuwa ƙasashen waje kuwa, an shawarce su da su yi rigakafin sannan kuma su san dokokin ƙasashen da za su je na yaƙi da korona kafin su tafi.